Yan mata tagwaye da aka sace a zamfara yayin da suke shirye-shiryen auren su
Barayin sun sace Hassana da Husainan ne a garin Dauran dake karamar hukumar Zurmi na jihar Zamfara a karshen makon da ya shude.
Masu garkuwan sun sace Hassana da Husainan ne a garin Dauran dake karamar hukumar Zurmi na jihar.
Kamar yadda rahotanni suka bayyana, an sace tagwayen ne tdakanin ranar Asabar da Lahadi na makon da ya shude.
Mataimakin shugaban karamar hukumar Zurmi, Abubakar Muhammad, ya shaida ma BBChausa cewa masu garkuwan sun bukaci a biya su Naira miliyan 100 kafin su sako tagwayen.
Yace tagwayen suna cikin mutane bakwai daga karamar hukumar da barayi suka sace kwana-kwanan nan.
Abubakar yayi kira ga yan Najeriya da su kawo masu dauki domin kawo karshen matsalar da suke fuskanta.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng