Saraki ya rantsar da sabbin sanatoci
Ahmed Babba-Kaita da Lawal Gumau sunyi nasarar lashe zaben cike gurbi da aka gudanar a jihar Bauchi da Katsina cikin watan Agusta.
An rantsar dasu a zaman da majalisar tayi ranar 10 ga watan Oktoba.
Sanatocin sunyi nasarar lashe zaben cike gurbi da aka gudanar a jihar Bauchi da Katsina.
Ahmed Babba-Kaita yayi nasarar lashe zaben cike gurbin da aka gudanar a watan Agusta na wakiltar arewacin jihar Katsina karkashin jam'iya mai mulki ta APC.
Ya doke dan uwan shi na jam'iyar PDP a zaben domin maye gurbin marigayi Bukar Mustapha a majalisar dokokin tarayya.
Shima Lawal Gumau yayi nasarar lashe zaben jihar Bauchi wanda aka gudanar ranar 11 ga watan Agusta karkashin jam'iyar APC.
Zai wakilci yankin kudancin jihar Bauchi a zauren majalisar dattawa bayan yayi nasarar maye gurbin marigayi Ali Wakili wanda ya rasu cikin watan Maris na 2019.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng