Majalisa ta tabbatar da Dan Iya a matsayin sabon mataimakin gwamnan Sokoto
Ibrahim Sarki ya bukaci sauran takwarorin sa da su tabbatar da sabon mataimakin gwamnan duba da kyawawan halayen sa.
An tabbatar da hakan ne sakamakon kudurin da mataimakin shugaban jam'iya mafi rinjaye, Alhaji Ibrahim Sarki ya shigar bayan da gwamna Aminu Tambuwal ya tura sunan Dan iya domin a tantance.
Bayan muhawara da aka yi kan kudurin, kakakin majalisar Alhaji Salihu Maidaji ya tabbatar da matsayin sabon mataimakin gwamna.
Mannir Dan-Iya zai maye gurbin tsohon mataimakin gwamnan jihar, Alhaji Ahmed Aliyu, wanda ya sauka daga mukamin a ranar 13 ga watan Nuwamba.
Tsohon mataimakin gwamnan ya sauka ne daga matsayin bayan da ya samu takardar tsayawa takarar gwamna na jam'iyar APC a zabe dake gabatowa.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng