ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Dan takarar shugaban kasa ya zabi yar  arewa a matsayin mataimakiyar sa

Zabin sa ta tabbatar da maganar da yayi a cikin watan Mayu na cewa zai zabi mace a matsayin wanda zata mara masa baya.

Khadijah Abdullahi-Iya

Durotoye ya sanar da labarin haka ne a shafin sa na twitter ranar laraba 21 ga watan Nuwamba.

Kamar yadda ya bayyana, Hajiya Khadijah ta kware  a bangaren tallafa wa jama'a inda tayi sama da shekaru 10 tana bayar da gudumawa ga al'ummar.

ADVERTISEMENT

Wa cece Khadijah Abdullahi Iya

Hajiya Khadijah Abdullahi Iya diya ce ga Alhaji Audu Bida wanda aka fi sani da Alhaji Audu Kongila da Hajiya Aisha Sherriff Usman.

Yar asalin karamar hukumar Bida dake jihar Neja amma haifafiyar yar Kaduna ce.

Tayi karatun digirin ta na farko a jami'ar Abuja inda tayi karatun ilimin shari'a. daga nan kuma ta kara karatun digiri ta biyu a jami'ar Jos shima a kan ilimin Shari'a.

Ta kafa cibiyoyi da gidauniyoyi domin tallafa ma karatun yara mara sa galihu a Kaduna da Abuja.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT