ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Masu liki a wajen biki zasu ziyarci gidan yari ko su biya N50,000 - inji CBN

Wanda aka kama da aikata laifin zai fuskacin hukuncin dauri a gidan kaso har tsawon wata shidda ko biyan N50,000 a matsayin kudin fansa.

Nigeria's Central Bank Governor Godwin Emefiele speaks during the monthly Monetary Policy Committee meeting in Abuja, Nigeria May 22, 2018.

Sanarwar da wani kwamitin babban bankin ta fitar ranar Alhamis, ta shaida cewa za'a kaddamar da wasu jami'ai wadanda zasu ringa rangadi domin kama tare da gurfanar da masu yi ma kudin Nijeriya cin fuska.

Kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito, mai magana da yawun bankin, Isaac Okorafor, ya tabbatar da cewa za'a baza jami'an masu rangadi a jihohi dake fadin kasar kuma zasu gudanar da aikin sa-ido tare rundunar yan sanda da taimakon ma'aikata na ma'aikatar shari'a.

Ya ja kunnen yan  Nijeriya cewa suyi hattara a wajen biki domin jami'ai zasu hallara domin lura da masu aikata laifi.

ADVERTISEMENT

Kakakin ya kuma yi gargadi na baki su dukufa wajen baiwa iyayen biki kyautar kudi ko makamancin haka a cikin takardar sirri.

Sanarwar ta kara da cewa masu yin rubutu a saman kudi zasu fuskanci hukunci dauri na wata shidda ko biyan diyar N50,000.

Bugu da kari babban bankin zata dau mataki ga masu siyar da kudi domin liki a wajen biki.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT