Advertisement
Dan kasuwa bai fidda rai wajen siyan kungiyar Arsenal, ya bada lokaci da zai dauki matakin yin haka
Tun ba yau ba attajirin wanda shine mafi kudi a nahiyar Afrika ya sanar da sha'awar siyan kungiyar take taka leda a gasar firimiya ta Ingila.
Advertisement
Shahararren attajirin dan kasuwa Alhaji Aliko Dangote tsaya kan bakan sa na siyan sanannen kungiyar kwallon kafa ta Arsenal dake Ingila.
Advertisement
A wata hira ta musamman da yayi da wakilin BBC, Dangote ya shaida cewa yunkurin siyan kungiyar tana nan sai dai amma za'a fara daukar matakin cikin shekarar 2020.
Yace a halin yanzu akwai wasu muhimman ayyukan da ya tasa a gaba wanda sai bayan ya kammala su zai bude wanann shafin.
"Yanzu muna da abubuwa muhimmai , kamar su matatar mai, kamar su kamfanin taki, kamar shimfidar bututun iskar gas, don haka lokacin da muke son siyan Arsenal shine a shekarar 2020" inji shi.
Mai kamfanin Dangote Group ya kara da cewa zasu fara magana da wadansu dake son su siyar da kason su a kungiyar.
Advertisement
Ya kara jaddada cewa a gaskiya ba yin haka shine muhimmin abun dake gaban su a halin yanzu.
Advertisement
Subscribe
Sportal WhatsApp
Latest Videos
Nigeria hausa
Gobara tayi sanad in mutuwar mutum 35
11.09.2018
Advertisement
Videos
Advertisement
Advertisement
More from Pulse Nigeria
Advertisement