Advertisement

Tsohon Gwamna yayi shelar tsayawa takarar shugaban jam'iyar APC

Ya Bayyanar da annjiyar sa na tsayawa takarar shugabancin jam'iya a wata taro ta musamman da aka shirya a garin Abuja
Advertisement

Ya dau alwashin hada kan jami'o'in gwamnatin kama daga bangaren shugabanci da majalisu.

Advertisement

Yayin da ya bayyanar da anniyar sa ga bainar jama'a a garin Abuja ranar alhamis 10 ga watan Mayu, Adam Oshiomhole yace zai tabbatar da samun nasara a ko da yaushe idan an zabe shi a matsayin shugaba.

Ya kara da cewa zai yi amfani da kwarewarsa a zamanin da yayi shugabancin kungiyar kwadago na NLC wajen shawo kan yayan jam'iyar.

Tsohon gwamna yana mai tabbatar da ma shugaban kasa da gwamnoni tare da yan majalisa cewa, ya na cike da kwarewa wanda cancanci ya zama jagoran jam'iyar mai ci.

Daga karshe, yayi ma jiga-jigai da iyayen jam'iyar bisa rawar da suka taka wajen raya jam'iyar da irin nasarori da suka samu.

Advertisement

Taron kaddamar da shelar takarar sa ya samu halartar gwamnan jihar Edo da yan majalisun jihar karkashin jagorancin kakakin majalisa tare da tsohon gwamnan jihar Bayelsa da Sanata Ita Enang da sauran su.

Advertisement
Latest Videos
Advertisement