ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Gwamnatin jihar Bauchi ta bada hutu ga ma'aikatan jihar

Gwamnatin ta bada hutun ne domin al'umar jihar su nuna farin ciki kan ziyarar aiki da shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kai jihar

Gwamna Abubakar Muhammed a cikin wata takardar sanarwa da hadimin sa na kafafen sada zumunta na zamani ya sa hannu, ya bayyana cewa an kaddamar da ranar hutun ne domin al'ummar jihar su tarbe shugaban da hannu biyu-biyu,

Gwamnan ya bukaci yan jihar da su fito a dandazon su domin yi ma shugaban maraba.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kai ziyarar aiki na kwana biyu jihar inda zai kaddamar da wasu ayyukan da gwamnatin Bauchi ta aiwatar.

Cikin ayyukan da shugaban zai kaddamar akwai shirin raba motor gona guda 500 ga manoman jihar.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT