ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Bayan ziyarar kwana shida da yayi zuwa kasar Sin shugaba Buhari ya dawo gida

Shugaban ya dawo ne bayan ziyarar da ya kai birnin Beijing domin halartar taron Forum on China-Africa Corporation (FOCAC) na 2018.

Shugaban ya bar kasar ne ranar asabar 1 ga watan Satumba zuwa kasar dake nahiyar Asiya domin hallatar taron gamayyar kasar Sin da Afrika.

A daren ranar Alhamis 6 ga wata jirgin shugaban ya sauka a garin Abuja.

Ya samu tarba yayin da ya sauka daga jirgi daga gwamnoni da wasu yan majalisar dattawa da ma'aikatan majalisar sa.

ADVERTISEMENT

Cikin su akwai mai girma gwamna Abubakar Muhammed na Bauchi da Gwamna Rochas Okorocha na Imo da Abubakar Badaru na jihar Jigawa.

A bangaren yan majalisa akwai Sanata Abdullahi Adamu da Sanata Aliyu Magatakarda wamako.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT