ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Dan wasan Nijeriya ya sauka kasar Scotland domin kammala yarjejeniya na komawa Rangers

Tun ba yau ba sabon kocin kungiyar Rangers ya nuna sha'awar da yake ma dan Nijeriya kuma ya sha alwashin kawo matashin kungiyar.

Kamar yadda jaridu suka bayyana, dan wasan zai koma kungiyar ne bisa yarjejeniyar aro daga kungiyar Roma na tsawon shekara daya.

Tun ba yau ba sabon kocin kungiyar Rangers ya nuna sha'awar da yake ma dan Nijeriya kuma ya sha alwashin kawo matashin dan kwallon kungiyar.

Tsohon gwarzon dan wasan kungiyar Liverpool yace hazikin matashin yana daya daga cikin dinbim yan wasa da suke birge shi. Ya yaba gwaninta da dan Nijeriyan ke nunawa a filin kwallo.

ADVERTISEMENT

Dan wasan ya sauka filin jirgin sama ta Edinbugh daidai karfe 10 na safiyar ranar Litinin 9 ga wata domin daukar matakai na karshe kan kwantiragin sa da kungiyar.

A rahoton da jaridar Daily Mail ta fitar, tauraron dan kwallon yana jiran takardar aiki na kasar gabanin sa hannu ga takardar kwantiragi.

Sadiq Umar wanda ke taka ma kungiyar As Roma na kasar Italiya wasa zai shiga cikin jerin sabbin yan wasan da sabon kocin Rangers ya kawo.

Kai ga yanzu kungiyar Rangers ta siyo yan wasa bakwai. ga sunayen su kamar haka: Scott Arfield, Allan McGregor, Jamie Murphy, Nikola Katic, Connor Goldson, Ovie Ejaria da Jon Flanagan.

Akwai yiuwar bayan Sadiq Umar shima dan wasan tsakiyar kasar Mali, Lassana Coulibaly, zai dawo kungiyar da taka leda bisa yarjejeniyar aro daga kungiyar Angers na kasar Faransa.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT