'Yan fashi sun kashe masu hakar gwal (waton zinare)
'Yan fashi sun kai hari a ƙauyen Bindin na ƙaramin hukumar Maru a Jihar Zamfara.
Gidan Jarida na Pulse ta tara labari cewa a ƙaramin hukumar Anka da Maru, ana yawan hakon maʼadinai kamar gwal da tantalite ba bisa ƙaʼida ba.
Daama,ʼYan fashi da makamai suna yawan kai hari a wuraren da ake tone-tonen ƙasa domin neman gwal. Wannan hari ya faru jiya a ranar litinin.
Kakakin ʼYan sanda na Jihar Zamfara DSP Muhammad Shehu ya tabbatar da wannan labari. Ya gaskanta cewa an tura maʼaikatan tsaro domin mayar da kwancen hankali bayan wannan masifa.
Gwanati ta na fama da hana ayukan masu bincikar ma’adinai ba tare da lasisi, ko kuma ba akan ƙa’ida ba.
Amma wannan mastala ta doge tun ba yau ba.
Daa muka kai wurin wannan masifa, ba mu tara da kowa ba a filin hakar ma’adinai.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng