ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Fittacen matashi ya samu karbuwa a PSG

Dan wasan ya gabatar da kanshi bainar masoyan kungiyar kuma yayi hira da manema labarai

Fitaccen matashi dan wasan kasar Faranasa ya samu karbuwa yayin da ya gabatar da kansa a bainar jama’ar sabon kungiyar sa.

Kylian Mbappe ya koma PSG daga Monaco a cinikin bashi wanda ake sa ran komawa na dindindin.

Matashin mai shekara 18 ya gana da manema labarai bayan ya samu karbuwa daga magoya bayan PSG.

“Ina mai farin  ciki shiga wannan kungiyar wanda take daya daga cikin kungiyoyin na duniya da suka shahara” maganar Mbappe yayin da aka gabatar dashi a filin parc des prince.

ADVERTISEMENT

Mbappe wanda ya gabatar da kanshi tare da iyalin shi yace zai zage damse wajen taimakon PSG da samun nasara.

Ana sa ran cewa dan kwallon zai bayyanar da kanshi a fili ranar juma’a  a wasan Ligue 1 da PSG zata yi da Metz.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT