ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Zan doke Buhari cikin ruwan sanyi a zaben 2019

Dan majalisar dattawan yayi wannan ikirari ne yayin da jirgin neman zaben sa ya kai ziyarar jihar filato ranar alhamis 27 ga watan satumba.

Rabiu Kwankwaso

Jagoran tafiyar Kwankwasiya yace yana da darajan kwato tutar mulki daga hannun jam'iyar APC a zaben gobe.

Yana mai cewa "idan na zama gwanin PDP , ni zan zama shugaban Nijeriya".

Kwankwaso yayi ikirari cewa yana da dinbim magoya a yankin arewa yamma kuma yawan su zai karu muddin jam'iyar PDP ta bashi damar zama dan takarar ta.

ADVERTISEMENT

Ya kuma soki gwamnati mai mulki ta APC inda yace ta gaza kawar da yunwa da rashin aikin yi da ake fama da ita a kasar.

Yayi alkawarin samad da ingantacciyar ayyukan cigaba da kuma tabbatar da tsaro tare da bunkasa harkar ilimi.

Yace zai kwatanta kwatankwacin tsarin ilimi na kyauta da yayi sanda yake gwamnan Kano idan ya zama shugaba.

Kwankwaso ya kuma yi alkawarin gina hanyoyi da gadaje domin tallafawa safarar mutane da kaya.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT