ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Minista ta doke danta wajen zama gwanin APC a jihar Yobe

Rahotanni daga jihar na nuna cewa duk da matsin lamba da jama'a suka yi masa na janye takarar sa ma matar mahaifin sa, Muhammed yaki amince da yin haka.

Baturen zaben fidda gwani da jam'iyar APC ta gudanar a jihar, Farfesa Abba Gambo, ya kaddamar da ita a matsayin wacce ta lashe zaben takarar kujerar ranar Laraba 3 ga watan Oktoba.

A zaben aka gudanar, Hajiya Khadija ta samu kuri'u mafi rinjaye inda ta samu 1295 yayin da shi kuma danta, Muhammed Ibrahim, ya samu kuri'u 15.

Kamar yadda muka samu labari, sauran yan takara biyu dake neman kujerar, Alhaji Abdullahi Kukuwa da Alhaji Ahmed Buba, sun janye takarar su domin baiwa ministan dama.

ADVERTISEMENT

Ministan ta kuma yaba masu bisa halarcin da suka yi mata.

Uwargidan tsohon gwmnan jihar Yobe zata daga tutar APC a zaben 2019 a takarar majalisar wakilai na tarayya.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT