ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Kalli dandazon jama'a da suka tarbi shahararren dan wasan Nijeriya a kasar Saudiya

Ahmed Musa ya sauka filin jirgin saman King Khaled dake nan birnin Riyadh ranar alhamis inda ya samu kyakkyawar tarba daga dinbim masoya dake jiran sa.

Dandazon masoyan fitaccen dan wasan Nijeriya suka garzaya filin jirgin sama domin yi ma sabon dan wasan kungiyar Al-nassr maraba.

A cikin wata faifan bidiyo da sabon kungiyar dan wasa ta fitar a shafin ta an kafafen sada zumunta, an gan inda magoya bayan kungiyar ke murna tare da yi masa waka.

Tsohon dan wasan Kano Pillars zai nemi ya kafa tarihi a sabon kungiyar shi cikin shekaru hudu kamar yadda kwantiragi cinikin shi ta bayyanar.

ADVERTISEMENT

Dan wasa mai tauraro ya koma kasar larabawa da taka leda bayan yarjejeniyar da kungiyar tayi da tsohon kungiyar shi na kasar Ingila na siyan shi a kan farashi wanda ba'a bayyanar. Sai dai ana hasashe miliyoyin kudi ne.

Ya bar kungiyar Leicester bayan shekara biyu da murza musu leda. Sai dai cikin shekaru biyun da yayi ya koma tsohon kungiyar shi ta CSKA Moscow bisa matakin aro gabanin kammala kakar 2017/2018.

Kungiyar Al-nassr ita ce ta zo na uku a gasar kakar da ta shude, ana kyautata zaton zata taka rawar gani a gasar bana bisa ga taimakon dan Nijeriya wajen saka kwallaye a ragar abokan adawar su.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT