ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Boko Haram ta kashe ma'aikaciyar jin kai, tayi barazanar kashe Leah Sheribu

Ta kara da cewa zuwa nan da wata daya za'a halaka ma'aikaciyar raino da unguwarzoman dake garkame a hannun su.

Mayakan sun sace ma'akaciyar cibiyar mai suna, Saifura Hussaini Khorsa, a cikin watan Maris na 2018 yayin da suka kai hari shingen sojoji a garin Rann na jihar Borno.

Kamar yadda rahotanni  suka bayyana akalla mutum takwas suka rasu sakamakon harin cikin su har da sojoji da ma'aikatan kiwon lafiya da wani likitar UNICEF.

Kungiyar ta daura alahkin kisan da tayi ga gwamnatin Nijeriya bayan da ta tura mata sakon kuma kai ga yanzu ba'a mayar da amsa ba.

ADVERTISEMENT

A rahoton da The Cable ta fitar, kungiyar tace ta tura sakon murya ga gwamnati amma gwamnatin tayi kunnen kashi ga sako shiyasa suka tunatar jama'a ta hanyar bindige ma'aikaciyar.

Bugu da kari kungiyar tace zata hada da yar makarantar Dapchi daya tilo dake hannun su har yanzu.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT