Advertisement
Mataimakiyar gwamnan Legas ta juya masa baya, tana goyon bayan abokin takarar sa
Hakan ya fito yayin da jam'iyar APC reshin jihar take gudanar da zabe na tantance wanda zai jagoranci jam'iyar a zaben gwamna na 2019.
Advertisement
Mataimakiyar gwamnan jihar Legas, Idiat Adebule, ta nuna goyon bayan ta da abokin takarar mai gidan ta na zaben fitar da gwanin jamiyar APC.
Advertisement
Sakamako dake fitowa daga wasu mazabu na jihar na nuna cewa gwamna Akinwunmi Ambode na fuskantar zagon kasa inda babba abokin takarar sa kuma dan takarar da mafi yawancin jiga-jigan jam'iyar ke goyon baya, Babajide Sanwo-Olu,yayi zarra.
Hajiya Idiat ta bayyana ra'ayin ta game da wanda take goyon baya yayin da take kada kuri'a a mazabar ta dake nan Ward A na karamar hukumar Iba.
Tace "Jam'iya ta fitar da dan takara kuma nima shi zan mara ma baya".
Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu yi ma mataimakiyar gwamnan hidima da magoya bayan ta sun garzaya wajen kada kuri'a da fosta na mara ma Sanwo-Olu baya.
Advertisement
Subscribe
Sportal WhatsApp
Latest Videos
Nigeria hausa
Gobara tayi sanad in mutuwar mutum 35
11.09.2018
Advertisement
Videos
Advertisement
Advertisement