Advertisement

Jami'an tsaro sun kama wani dan kasuwa mai siyar da jakkuna wanda UNICEF ta baiwa yan gudun hijira na jihar Borno

Lamarin ya faru a kasuwar kofar wambai dake nan jihar Kano
Advertisement

Jami'an tsaro sun kama wani dan kasuwa dake siyar da jakkuna wanda asusun dake nema ma yara ilimi ta UNICEF ta bada domin tallafawa yaran yan gudun hijira dake jihar Borno.

Advertisement

Lamarin ya faru ne a kasuwar kofar Wambai dake nan jihar Kano.

Jami'in da ya jagoranci sammamen CSP Suleiman Aliyu Gusau ya shaida wa manema labarai cewa labarin sirri suka samu daga jama'a na cewa ana siyar da kayan tallafi da aka ware ma yan gudun hijira a kasuwar.

Shi dai dan kasuwar da aka kama ya bayyana cewa shima ya samu jakunan a tsari daga garin Maiduguri kan naira dari shidda (N600) kuma shi yana siyar dasu a kan N1200.

Advertisement
Latest Videos
Advertisement