ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Majalisar dokoki ta tsige kakakin ta

Dan majalisar, Mista Peter Ibrahim, yace sashe 92 na kundin dokar kasa ta 1999 ta bada damar yin haka.

Wannan matakin ya biyo bayan kudurin da dan majalisar mai wakiltar mazabar Barkin Ladi yayi.

Yace majalisar ta dauki wannan matakin bayan da yan majalisa masu goyon bayan tsige shi sun samu rinjaye. Kamar yadda ya bayyana yan majalisar sun tsige shi ne bayan zaben kin jini da suka gudanar kuma masu goyon baya suka samu rinjaye.

Sakamakon matakin da suka dauka dan majalisa, Yusuf Gagdi, ya fitar da  Mista Joshua Madaki mai wakiltar kudancin Jos a matsayin wanda zai gaje shi.

ADVERTISEMENT

Shima dan majalisar, Abdul Yanga ya amince da takarar Joshua a matsayin wanda zai maye gurbin wanda aka tsige wanda daga karshe majalisar ta tabbatar dashi a matsayi sabon kakakin ta.

A wani bangare kuma mutum 12 cikin 17 sun gudanar da zaben kin jini ga shugaban jam'iyar mafi rinjaye na majalisar. Yan jam'iyar na majalisar sun tsige Henry Yunkwap inda suka maye gurbin sa da Mista Na'anlong Daniel wanda ke wakiltar mazabar Mikkang na jihar.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT