ADVERTISEMENT
Mukaddashin shugaban kasa ya sallami shuguban DSS Lawal Daura
Matakin ya biyo bayan lamarin da ya faru a zauren majalisar dokoki inda jami'an DSS suka hana shiga da fita tare da tare hanyoyi
Wannan labari ya fito a cikin wata sanarwa da kakakin sa Laolu Akande ya fitar ranar talata 7 ga watan Agusta. Mai'akaci mai rike da mukami mafi girma a hukumar zai maye gurbin sa.
Sai dai sanarwar bata bayyana dalilin daukar wannan matakin da shugaba mai riko yayi ba, ana hasashe cewa korar ta biyo bayan lamarin da ya faru a zauren majalisar tarayya inda jami'an rundunar DSS suka mamaye zauren tare da hana ma'aikata da yan majalisar shiga.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
ADVERTISEMENT
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng
ADVERTISEMENT