Advertisement

Muhammadu Buhari a jamhoriyar Nijar

Shugaban ya ziyarci Kasar Nijar inda zai halarci taro ta musamman na majalisar kasashen yammacin afrika
Advertisement

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya iso jamhoriyar Nijar domin halartan taron na musamman  na ECOWAS a kan samad da tilon kudi na majalisar kasashen yammacin afrika.

Advertisement

Shugaban ya sauka Niamey babban birnin tarayyar kasar kuma ya samu tarba daga takwaran shi shugaba Mahamadou Issoufou.

Cikin tawagar shugaba Buhari da suka raka shi akwai ministan kudi Kemi Adeosun tare da gwamnan babban bankin Nijeriya Godwin Emefiele kamar yanda kakakin shugaban Femi Adeshina ya sanar.

Kasashen dake cikin wannan majalisar sun hada da Cote D'ivoire, Jamhoriyar Nijar, Ghana da Nijeriya.

Ana sa ran cewa Shugaban zai dawo Nijeriya bayan an kammala taron.

Advertisement
Latest Videos
Advertisement