Advertisement

Buhari ya jagoranci taron majalisar ministoci kwana daya da dawowa ƙasar

Shugaban ƙasa bai halarcin taron majalisar a mako da ta gabata sanadiyar tafiyar da yayi zuwa ƙasar Amurka
Advertisement

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranci taron majalisar ministoci ranar laraba 27 ga watan Satumba 2017.

Advertisement

Shugaban kasa bai halarcin taron majalisar a mako da ta gabata sanadiyar tafiyar sa zuwa ƙasar Amurka.

A makon da ya gabata mataimakin shugaban Yemi Osinbajo ya jagoranci taron kasancewa shugaban yayi tafiya domin halartar taron koli na majalisar dinkun duniya da aka yi a birnin New york.

A hanyar shi na dawowa ranar alhamis 21 ga watan Satumba shugaban ya yada zango a birnin London wanda mutane ke ganin cewa ya je ganin likitocin shi ne a can.

Buhari ya dawo Nijeriya ranar litinin 25 watan satumba

Advertisement
Latest Videos
Advertisement