ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Atiku babban dan siyasa ne, ficewar shi daga jam'iyar APC abun bakin ciki ne

A cewar shi, shi dai Atiku daya daga cikin masu ruwa da tsaki ne a harkar siyasa na kasa ne.

Atiku Abubakar ya sauya sheka zuwa jam'iyar adawa ta PDP inda ya samu damar zama mataimakin shugaban kasa na tsawon shekara takwas. Yace babban dalilin da ya sanya yafice daga jam'iyar shine rashin biyan bukatun yan kasar da jam'iyar APC ke fama da ita.

korocha ya fadi hakan ne ranar asabar 9 ga watan disamba yayin da ya amshi takardar karramawa a jami'ar Adekunle Ajasin dake nan jihar Ondo.

Gwamnan ya bayyana cewa ficewar Atiku daga APC abun bakin cikin ne ga jam'iyar shi domin shi kasurgumin dan siyasa ne wanda kowa zai yi alfahari dashi.

Daga baya dai Okorocha ya kara da cewa jam'iyar mai ci ta APC zata iya bakin kokarinta wajen maye gurbin sa a cikin jam'iyar.

ADVERTISEMENT

Gwamnan yayi tsokaci game da jawabin da jigon jam'iyar APC yayi watau Bola Tinubu inda yake cewa Shugaba Buhari ba zai samu tikitin zarcewa a zaben 2019.

Shi dai gwamnan yace yana bayan shugaban dari bisa dari domin zarcewa a karagar mulkin kasa.

Duk da cewa Buhari bai fitar da kuddirin tsaya takarar zarcewa, akwai kwakwarar alama mai nuna cewa zai fitar da anniyar sa nan gaba.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT