Shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, ya rantsar da sabbin Sanatoci Ahmed Baba-Kaita da Lawal Gumau shigar su farfajiyar majalisar.
An rantsar dasu a zaman da majalisar tayi ranar 10 ga watan Oktoba.
Sanatocin sunyi nasarar lashe zaben cike gurbi da aka gudanar a jihar Bauchi da Katsina.
Ahmed Babba-Kaita yayi nasarar lashe zaben cike gurbin da aka gudanar a watan Agusta na wakiltar arewacin jihar Katsina karkashin jam'iya mai mulki ta APC.
Ya doke dan uwan shi na jam'iyar PDP a zaben domin maye gurbin marigayi Bukar Mustapha a majalisar dokokin tarayya.
Shima Lawal Gumau yayi nasarar lashe zaben jihar Bauchi wanda aka gudanar ranar 11 ga watan Agusta karkashin jam'iyar APC.
Zai wakilci yankin kudancin jihar Bauchi a zauren majalisar dattawa bayan yayi nasarar maye gurbin marigayi Ali Wakili wanda ya rasu cikin watan Maris na 2019.