ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Jawabin Shugaba Buhari a taron ƙasashen ECOWAS da ya halarta a jamhoriyar Nijar

Shugaban yayi jan hankalin ga sauran ƙasashen ECOWAS game da kalubalen da kasashen turai suka fuskanta yayin da suke neman kafa irin manufar da suke nema

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya dawo gida Nijeriya bayan ya ziyarci garin Niamey babban birnin jamhoriyar Nijar domin halartan taron kasashen ECOWAS a kan amfani da kudi na bai daya da kasashen.

Babban mataimakin shugaban a kan duniyar gizo Bashir Ahmad ya sanar da dawowar sa a shafin sa na twitter yammacin ranar talata.

Kasashen da suka halarci zaman taron na kan amfani da kudi na bai daya ga kasashen ECOWAS sun hada da Cote D'ivoire, Ghana, Jamhoriyar Nijar da Nijeriya.

A jawabin sa wajen taron shugaba Buhari yayi kira ga kasashen ECOWAS da su bi a hankali wajen samad da anniyar su na amfani da kudi bai daya tsakanin su.

ADVERTISEMENT

Shugaban yayi jan hankalin ga sauran kasashen ECOWAS game da kalubalen da kasashen turai suka fuskanta yayin da suma suke neman kafa wannan tsarin.

Ya kara da cewa Nijeriya baza ta sa hannu a kan tsarin tafiyar da al'amarin kudi na kasashen ECOWAS alhali akwai matsololi da suka fi shi muhimmaci ko suka fi zama abun yi cikin gaggawa.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT