Gwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai ta tabbatar ma al’ummar jihar kaduna cewa babu riƙicin da zai ɓarke jihar.
ADVERTISEMENT
Akwai zaman lafiya a jihar Kaduna kuma mun ɗau matakai na kare mutane da dukiyoyin su
Gwamnan ya tabbatar ma mazaunin jihar cewa babu tarzoman da zai barke a jihar
A wata takarda da kakakin sa Samuel Aruwan ya fitar ranar alhamis 14 ga watan Satumba gwamnan yace al’ummar jihar su cigaba da ayyukan su ba tare da fargaba.
Gwamnan yace hukumomin tsaro sun ɗauki matakai na kare mutane da duƙiyoyin su.
El-rufai yace a irin wannan lokacin da tarzoma ke neman ɓarkewa a wasu jihohi ya kamata al’ummar jihar su ɗaukaka zaman lafiya.
ADVERTISEMENT
Gwamnan dai yace gwamnati baza ta lamunta da kalamun tunzura kuma al’ummar jihar su tabbatar da labari kafin su yaɗa.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
ADVERTISEMENT
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng
ADVERTISEMENT