ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Hukuma ta kama wata mahaifiyar yara 7 mai fataucin ganyen wee-wee

Wakawa yace an kama matar wanda asali mazaunin jihar oyo ce a hanyar Uzebba-ifon da ganyen yayin da take kokarin komawa jihar Oyo.

Hukumar dake kula da dokar hana miyagun kwayoyi ta NDLEA ta kama wata yar shekara 50 mahaifiyar yara 7 wanda ta boye ganyen wee wee mai kimanin kilo 40 a cikin kayan tsiro.

Shugaban hukumar ta reshin jihar Edo Mista Buba Wakawa ya tabbatar da kamun da suka yi ma manema labarai a garin Benin ranara talata.

Wakawa yace an kama matar wanda asali mazaunin jihar oyo ce a hanyar Uzebba-ifon da ganyen yayin da take kokarin komawa jihar Oyo.

Yace sun gano ganyen cikin wasu buhuna hudu tare da na ganyen kabewa wanda dashi take bogi domin kada ayi bincike akan kayan da take safara.

ADVERTISEMENT

Jami'in yace hukumar ta fara bincike ta musamman domin gano masu safarar miyagun kwayoyi musamman na tsiro.

Yayin da take amsa laifi, matar wanda ake zargi tace auren ta ya mutu kuma tana neman kudi domin biyan kudin jarabawa ta WAEC ma yaran ta shiyasa ta aikata laifin.

Shi dai kwamandar yace za'a gurfanar da ita ga kotu kana za'a kama abokanan aikin ta.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT