Hukumar aikin hajj na ƙasa NAHCON tace yan Nigeria guda 5 suka rasu tun da aka fara hajjin bana
Mutum 5 sun rasu yayin da wata ta haifi yaro a cikin alhazan Nigeria
Shugaban hukumar alhazai na kasa ya sanar da haka a wani taro da hukumar ta gudanar ranar talata a Makka
Shugaban hukumar Alhaji Abdullahi Muhammed ya sanar da haka a wani taro da hukumar ta shirya don shirya ma ranar Arafa a Makka ranar talata.
Shugaban bai bayyanar da sunayen wadanda suka rasu amma ya sanar cewa hukumar zata tuntubi iyalen su kafin ta fitar da sunayen su.
Hukumar ta sanar cewa ta samu karban haihuwa daya kuma an samu wata wanda tayi farin ciki kuma tana tabbatar ma alhazan cewa hukumar zata cigaba da taimakawa alhazan wajen kiwon lafiya har a gama aikin hajjin.
Muhammed yayi kira ga ma’aikatan hukumar da su tashi tsaye wajen ganin cewa anyi aikin hajjin bana cikin sauki kuma dukkanin alhazan Nigeria sun koma gida cikin lafiya.
Mutum 81,200 daga Nigeria suka tafi aikin hajjin bana kuma akalla mutanbe sama da miliyan 2 zasu yi aikin wannan shekara.
Za’a fara aikin bana ranar laraba 30 ga watan agusta.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng