ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Shugaba Buhari ya nada Bola Tinubu jagoran kwamitin neman sulhu

Kwamitin sulhu da shugaban ya kafa zata nemi hanyoyin hada kan yan jam'iyar APC domin cinma burin manufar jam'iyar.

Kakakin shugaban kasa Garba Shehu ya sanar da haka a shafin sa na twitter ranar talata 6 ga wawatn yau.

Tsohon gwamnan jihar Legas kuma jigon jam'iyar mai ci Bola Tinubu zai jagoranci wannan kwamitin neman sulhu domin magance rikici dake tsakanin yan jam'iya da ma shigabanin jama'a har da wasu dake rike da mukamai siyasa a jihohi daban daban na kasar.

Wannan matakin da shugaban ya dauka na neman sulhu tsakanin yan jam'iyar shi ya fito ne bayan sukar da tsofafin jagorarin kasar Olusegun Obasanjo da Ibrahim Babangida suka yi masa kan ya jingine batun neman zarcewa a zaben 2019.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT