ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Ƙungiyar matasa sun ƙalubalanci shugaban kasa da ya yi murabus cikin maƙonni 8

ƙungiyar tace matasa miliyan bakwai zasu tsige shi daga mukamin shi idan bai yi murabus

Nigerian President Muhammadu Buhari has been on medical leave in London since the beginning of May

Wata ƙungiyar matasa mai suna ‘matasan nijeriya masu neman adalci’ watau “Nigerian Youth Advocate for Justice” sun ƙalubalanci shugaba Muhammadu Buhari  da yayi murabus kasancewar barin kasar da ya yi har kwana 53.

Ƙungiyar ta ba shugaba makonni 8 da ya yi murabus ko kuma matasa miliyan 7 daga jihohi 22 zasu tsige daga mukammin shi.

Shugaban ƙungiyar, Seriki Olorunwa yace, rashin lafiyar shugaban kasa yasa ba zai iya cigaba  da mulkin kasar.

“Muna kira ga majalisar dattawa, majalisar wakilai, majalisun jihohi da sauran su da su yunkura wajen ganin cewa shugaba ya yi murabus don amfanin yan kasa.’ Olorunwa yace.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa matasa a shirye suke wajen cimma buri su har ma ya bada tabbaci cewa wannan zai faru ba tare da zubar da jini.

Dangane ga kashe-kashe, garkuwa da mutum da kuma sace-sace dake yaduwa a kasar, ƙungiyar tace jam’iyar APC ta wulakanta yan nijeriya don son kai.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT