Shugaban ya sauka a filin jirgin Murtala Muhammed dake nan jihar inda ya samu tarba daga gwamna Akinwunmi Ambode da sauran jami'an gwamnati safiyar ranar alhamis 29 ga watan maris.
ADVERTISEMENT
Ziyarar shugaban kasa zuwa jihar Legas
Wannan shine karo na farko da shugaban kasa mai zaman kujera zai kai ziyarar aiki jihar Legas
Jim kadan bayan saukar sa shugaban ya kaddamar da sabuwar tashar mota na zamani da gwamnatin jihar ta gina a nan garin Ikeja babban birnin jihar.
Shugaban zai kuma halarci taron lekca na raya zagayowar ranar haihuwar tsohon gwamnan jihar kuma daya daga cikin jagororin jam'iyar APC wato Asiwaju Bola Tinubu wanda za'a gudanar a dakin taro na Eko convention center dake garin Victoria Island nan jihar.
ADVERTISEMENT
Wannan shine karo na farko da shugaban kasa mai zaman kujera zai kai ziyarar aiki jihar Legas.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
ADVERTISEMENT
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng
ADVERTISEMENT