Zamu goyi bayan duk wani dan takara da ya zama gwanin PDP
Tsohon gwamnan jihar Sakkwato ya sanar da hakan ne yayin da ya gana da manema labarai a garin Bauchi ranar Lahadi 23 ga wata.
Bafarawa yace ba matsala bane ganin cewa cikin yan takarar zama gwanin jam'iya akwai gwamnan jihar sa, Aminu Waziri Tambuwal, domin sun sha alwashin mara ma duk wanda yayi nasara baya a zaben.
Yace babban burin su shine su kwato kujerar mulkin kasa daga jam'iyar mai mulki ta APC.
Tsohon gwaman ya kara da cewa bai shigo siyasa don neman kudi, yace ya shigo ne domin yayi wa al'umma aiki kuma yana ganin shi yafi cancanta domin yana kwarewa a harkar siyasa duba da shekaru takwas da yayi a matsayin gwamnan Sakkwato.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng