ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Za'a bude da ofishin neman tazarcen Shugaba Buhari a garin Ibadan

Za'ayi taron kaddamar da wannan ofishin a babbar wurin taro dake jami'ar Ibadan a daidai karfe 11 na safe.

Ministan sadarwa Adebayo Shittu ya kirkiri wannan ofishin karkashin kungiya mai taken Buhari/Osinbajo Dynamic Support group.

A cikin takardar sanarwa da ministan ya fitar, tsohon gwamnan jihar Abia Orji Uzo Kalu zaiyi jawabi a wajen taron.

Manyan baki da zasu halarci wajen taron sun hada da jigon jam'iyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da tsohon shugaban majalisar dattawa Ken Nnamani da tsohon ministan man fetur Don Etiebet da kuma gwamnan jihar Oyo Abiola Ajimobi wanda shine jagoran taron.

Hakazalika ministan safuri Rotimi Amaechi da tsohon shugaban jam'iyar APC mai rikon kwarya Bisi Akande zasu halarci wajen taron.

ADVERTISEMENT

A bangaren gwamnoni kuma akwai gwamnan jihar Kaduna da Osun da ta Ondo har da ta jihar Legas kamar yadda ya sanar a takardar da ya fitar.

Cikin jerin yan majalisa da zasu halarci bikin kaddamarwa akwai Sanata Abu Ibrahim mai wakiltar kudancin jihar Katsina tare da sanata Ali Ndume da sanata Ayo Akinyelure.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT