ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Tawagar yan wasan kwallon Nijeriya zasu buga wasan su na gaba a garin Kaduna

Tawagar yan wasan zasu kece raini da na kasar Libya cikin jerin wasanin neman shiga gasar kofin Afrika da za'a buga shekara mai zuwa.

Wannan shine karo na farko da tawagar zata yi amfani da filin bayan wasan ta ta da tawagar kasar Masar a cikin shekarar 2016.

Zaben filin ya biyo bayan binciken da kocin tawagar yan wasan Gernoht Rohr yayi.

NFF tace ta sanar ma hukumar kwallo ta Afrika game da wajen da za'a buga wasan kuma bisa ga binciken da kocin Nijeriya yayi a filin duk wata gyara da ya kamata a yi za'ayi shi gabanin wasan.

ADVERTISEMENT

Tawagar yan wasan zasu kece raini da na kasar Libya cikin jerin wasanin neman shiga gasar kofin Afrika da za'a buga shekara mai zuwa.

Nijeriya zata buga wasan ta na uku na rukunin D da da kasar arewacin afrika ranar 10 ga watan Oktoba.

Wasan ta na farko Nijeriya ta fadi inda kasar Afrika ta kudu ta doke ta da ci biyu babu. Wasan ta na Biyu Nijeriya ta lallasa kasar Seychelles da ci uku babu ko daya.

Tawagar zasu nemi su tabbatar da matsayin su domin shiga gasar afrika da anniyar samun galaba akan Libya.

A halin yanzu Nijeriya ce na uku a rukunin D da maki uku yayin da Libya da Afrika ta kudu suka raba maki hudu hudu kuma suka zama na jagororin rukunin.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT