ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Yan sanda sun gayyaci dan takarar gwamna kan zargin magudin jarabawa kwana uku gabanin zabe

Ademola Adeleke yana daya daga cikin yan takarar gwamnan jihar Osun a zaben jihar da za'a gudanar ranar asabar 22 ga watan Satumba.

Senator Ademola Adeleke

A labarin da Channels Tv ta fitar ana zargin dan takarar da kulla makarkashiya da wasu mutane hudu yayin rubuta jarabawar a shekarar 2017.

Tsohon dan majalisar dattawa wanda zai fito karkashin jam'iyar PDP yayi suna a kasar duba da faidan bidiyo din shi yayin da yake tika rawa yake yawan mamaye kafafen sadarwa.

Hakazalika dan siyasan ya shahara sakamakon dangantarkar shi da fitaccen mawakin Nijeriya wato Davido.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar yan sanda na kasa Jimoh Moshood, ya sa hannu, ana zargin Adeleke da yin zaman jarabawar NECO ta hanyar sajewa a madadin wani dalibin makarantar Ojo/Aro Community High Schoo dake jihar Osun a cikin shekarar 2017.

Duk da cewa dan takarar yana da shekaru 57, sanarwar ta bayyana cewa ya karyata labarin shekarun sa kamar yadda hukumar NECO ta bayyana.

An zargi Adeleke da rage shekarar haihuwar sa zuwa 1997.

Rundunar yan sanda na neman sa tare da sauran mutane hudu da ake zargin sun taimaka masa wajen aikata laifin domin su gabatar da kansu a ofishin su dake garin Abuja domin a gabatar dasu gaban kotu.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT