ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Wani matashi ya hau bene ba tare da fargaba domin ceto rayuwar jariri

Dan kasar mali wanda ya koma Faransa ya nuna bajinta wajen ceton rayuwar wata jaririya da ta makale a bene mai dogon tsawo

Lamarin ya faru ne a yankin Northern Paris na babban birinin kasar a ranar asabar 26 ga watan Mayu.

Dan asalin kasar Mali ya nuna bajinta wajen yin haka inda ya hau benaye da dama kafin ya kai ga inda jaririyar take.

jama'a da dama sun yaba masa bisa kokarin da yayi wajen yin nasarar kubutar da jaririyar.

Mamoudou Gasama wanda ke da shekaru 22, ya bayyana cewa yayin da yake yunkurin ceto rayuwar ta, bai yi la'akari ko tunanin rayuwar sa.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda ya shaida ma yan jarida gabanin lamarin, matashin yace sai bayan ga ya ceci rayuwar diyar yayi ta kyarma.

Bisa bajinta da ya nuna, shugaban garin Paris tayi masa kira ta musamman domin mika godiyan ta tare da yi masa kyakkyawar albishir.

Bugu da kari matsahin ya hadu da shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron inda shugaban ya mika masa takardar zama dan kasa tare da bashi aiki a hukumar agaji dake kashe gobara ta kasar.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT