Gwamanan jihar Kano Abdullahi Ganduje ya sha da kyar harin da ƴan fashi suka kai mai a hanyar Abuja zuwa Jos.
Gwamnan jihar kano ya sha da ƙyar harin da ƴan fashi suka kai mai
Yan fashi da makami sun kai ma gwamnan harin kwantan ɓauna amma basu samu nasara ba inda jami’an tsaro na gwamnan suka yi hartabo dasu
A bisa labari da jaridar Guardian ta fitar, yan fashi sun kai ma gwamnan harin ƙwantan ɓauna amma basu samu nasara ba sanadiyar hartabon da suka yi da jami’an tsaro na tawagar gwamnan.
Rahoto ya nuna cewa anyi ɓarnar wutar bindiga tsakanin yan fashin da jami’an tsaro sama da sa’o’i biyu ranar alhamis 5 ga watan octoba.
Kakakin gwamnan Malam Tanko Yakasai ya tabbatar da harin ga manema labarai.
A bayanin wani shaidar gani da ido, da taimakon jami’an tsaro na daga cikin tawagar shi gwamnan ya sha daga harin da yan fashin suka kai.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng