ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Sunayen jami'o'in gwamnati da shugaban kasa ya nada

Ga sunayen sabbin jami'an da shugaba buhari ya nada tare da hukumar su kamar haka

Shugaban yayi nadin ne ranar alhamis 24 ga watan mayu.

Ga sunayen sabbin jami'an da ya nada tare da hukumar su kamar haka:

Dokta Anasa Ahmad Sabir - an nada shi a matsayin babban daraktan asibitin koyarwa ta Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto.

Dokta Theresa Obumneme Okoli wadda ya nada a matsayin sabon shugaban kwalejin gwamnatin tarayya dake horas da malamai dake nan garin Umunze na jihar Anambra.

ADVERTISEMENT

Sai kuma Dokta Emmanuel Ikenyiri wanda ya nada a matsayin shugaban Kwalejin Gwamnatin Tarayya dake horas da malamai na garin Omoku a jihar Rivers.

Wannan sabbin nade-nade da yayi ya biyo bayan wanda ya yi a farkon watan mayu. Shugaban yayi nade-naden ne a hukumar NDIC da kuma hukumar zabe ta kasa.

Cikin wadanda ya nada a hukumar NDIC akwai babban lauya, Festus Keyamo wanda ya kaddamar a matsayin kakakin yakin neman zaben sa.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT