Shugaban ya dawo birnin tarayya a daren ranar alhamis 3 ga watan Mayu.
Shugaba Buhari ya dawo Nijeriya bayan ziyara da ya kai Amurka
Shugaban ya dawo birnin tarayya a daren ranar alhamis 3 ga watan Mayu
Manyan jami'an majalisar sa da jami'an tsaro sun tarbe shi a filin jirgin sama yayin da ya sauka.
Shugaban dai ya dawo bayan kwana biyu da barin kasar Amurka. Fadar sa ta sanar cewa ya yada zango birnin London ne bisa wani dan gyara da aka yi ma jirgin dake tafiye dashi.
A ganawar da yayi da shugaban Amurka, shugabannin sun tattauna kan hanyoyin bunkasa harkar kasuwanci tsakaknin kasar Nijeriya da Amurka tare da hanyoyin kawo karshen ta'adanci.
Bayan ganawar da yayi da Donald Trump, shugaba Buhari ya gana da wasu yan kasu yan kasar Amurka kan yadda zasu zuba jari a kasar Amurka.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng