A karar da ofishin ma'aikatar shari'a na tarayya ta shigar ranar 31 ga watan janairu 2018, ana zargin Dino Melaye da bada shaidar karya ga mataimakin gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello mai suna Edward Onoja David tare da bada labari karya mara inganci.
ADVERTISEMENT
Sanata ya mayar ma gwamnatin tarayya martani da wannan hoton izgili kan karar da shigar a kan sa
Dan majalisar mai wakiltar yammacin jihar Kogi ya mayar da martani ga gwamnatin tarayya cikin izgili a wani sako da ya wallafa a shafin sa na kafar sada zumunta.
A hoton za'a gan inda dan majalisar ya sa yatsan hannayen sa ga idanuwa tare da rubuta "FG Vs Dino Melaye".
ADVERTISEMENT
Wannan ya nuna cewa dan majalisar ya shirya damawa a gwamnati kan karar da ta shigar akan sa ko kuma izgili ne na tsokane wanda ya saba yi?
Idan ba'a manta ba bara wannan dan majalisar yayi kaurin suna a shafukan sada zumunta sakamakon bidiyon wakar izgilanci da ya fitar ga wadanda yake zargin cewa makiyan shi ne.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
ADVERTISEMENT
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng
ADVERTISEMENT