ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Nijeriya da Faransa sun rattaba hannu ga yarjejeniyar $475M

yarjejeniyar zata taimaka wajen bunkasa ayyokan zamani a jihar Legas da Kano da Ogun.

Hakan ya faru ne yayin da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ya ziyarci fadan shugaba Muhammadu Buhari sakamakon ziyarar kwana biyu da ya kawo Nijeriya.

Yarjejeniyar zata taimaka wajen bunkasa harkokin sufuri a jihar Legas tare da inganta hanyoyin inganta shuka a jihar Ogun da samad da hanyoyin tafiyar ruwa a jihar Kano.

Ministan kudi, Kemi Adeosun, ta rattaba hannu a takarda a madadin gwamnatin jihohin da yarjejeniyar zata amfana a fadar shugaban kasa ranar talata 3 ga wata.

ADVERTISEMENT

Gabanin  yarjejeniyar shugabannin sun tattauna kan wasu muhimman batutuwa wanda ya danganci bunkasa harkokin kasuwanci da inganta tsaro.

Macron, ya bayyana cewa gwamnatin sa zata taimaka wajen yaki da ta'adancin yan ta'adar boko haram da ISIS da suka addabi al'ummar kasar da sauran kasashen yammacin nahiyar Afrika.

Daga karshe shugaba Buhari, yayi ma matashin shugaban Farsansa godiya bisa taimako da goyon baya da yake wajen kawar da ta'adanci a kasar da sauran kasashen Afrika.

Bayan ganawar shi da shugaban kasa, Emmanuel Macron ya garzaya jihar Legas inda ya halarci wani taro na musamman na raya al'ada a daidai wajen taro da aka gina don mutunta fitaccen mawaki Marigayi Fela Kuti dake nan jihar Legas.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT