ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Jagoran yan wasan Super eagles ya nuna godiya bayan kubutar da mahaifin shi da masu garkuwa da mutane suka yi

Rahotannin sun nuna cewa an sace mahaifin sa ne hanyar sa zuwa jihar Enugu dake kudancin Nijeriya daga jihar Benuwe.

Kamar yadda dan wasan ya bayyana, labarin sace mahaifin shi ya kai ga kunnen shi sa'o'i gabanin wasan Nijeriya da Argentina a gasar kofin duniya.

Rahotannin sun nuna cewa an sace mahaifin sa ne hanyar sa zuwa jihar Enugu dake kudancin Nijeriya.

A wata takardar sanarwa da rundunar yan sanda ta jihar Enugu ta fitar, jami'an rundunar sunyi nasarar kubutar da mahaifin dan wasan ranar 2 ga watan Yuli daidai karfe 2 na rana.

ADVERTISEMENT

Sakamakon kokarin da rundunar yan sanda suka yi, Mikel Obi ya jinjina masu tare da yi masu godiya.

Ga sakon da ya rubuta a shafin sa na twitter kamar haka "Ina mai mika godiya ga jami'an tsaro da suka kubutar da mahaifina bayan lamarin da ya faru cikin satin nan".

Bugu da kari tsohon dan wasan tawagar kungiyar Chelsea dake Ingila, ya yi dinbim yan kasa da suka taya shi jaje tare da mara masa baya.

Lamarin dai shine karo na biyu da masu garkuwa da mutane suka saci mahaifin shahararren dan kwallon. Karo na farko ya faru a cikin shekarar 2011.

Tuni dai dan wasan ke ta samu jinjina da yabo daga yan kasa a kafafen sada zumunta da kafofin watsa labari bisa bajinta da ya nuna wasan Nijeriya da Argentina duk da ya san cewa anyi awon gaba da mahaifin shi.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT