ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Matar dan wasan super eagles ta karyata labarin dake yaduwa na cewa mijinta ya lakada mata duka

A labarin da ya fito ranar lahadi, ana zargin dan wasan da raunata uwardakin sa bayan rashin jituwa da suka samu a gidan su dake nan jihar Sakkwato.

A labarin da shahararren kafar watsa labarai Instablog ta fitar, an zargin mai tsaron bayan tawagar nijeriya daga hannu ma matar sa bayan rashin jituwa da suka samu bisa ga kin amsa kiran waya.

Kamar yadda labarin ya fito, lamarin ya faru ne a nan gidan su dake jihar Sakkwato ranar lahadi 15 ga wata.

ADVERTISEMENT

Labarin ya mamaye kafafen sada zumunta inda ya zamanto batun muhawara a dandalin. Jama'a da dama sun nuna bacin ran su ga lamari tare da yin Allah-wadai ga mazaje masu dukar matan su.

Sumayya Mustapha ta karyata labari

Sai uwardakin dan kwallon ta karyata wannan labarin ranar litinin 16 ga watan Yuli.

A labarin da mujallar Tozali ta fitar, Summaya tace babu abun da ya faru tsakaninta da mijinta kuma labarin dake yaduwa na cewa tasha duka a hannun maigidanta ba gaskiya bane.

Uwardakin Sumayya Mustapha ta yaba so da kauna da suke da dan kwallon tare da jinjina masa bisa kulawarn da yakje nuna mata.

ADVERTISEMENT

Dangane da hoton rauni da ta samu a ido, tace lamarin ya faru ne tun kwanakin baya kuma ta same shi ne sakamakon hatsari da ta samu.

Daga karshe ta kira lamari da jarawaba daga Allah domin a cikin duk wata falalar da mutum ya samu akwai jarabawa dake tare da ita.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT