Wannan labarin ya fito ne a wata wasika da ya fitar ranar 16 ga watan Mayu.
Mataimakin gwamna yayi murabus
Yace matakin aje aikin da yayi ya biyo bisa nisantar da kansa daga bugawa da giyan kujeran siyasa.
A wani rahoto da gidan telebijin. Channels ta fitar, Mataimakin gwamnan ya mika takardar murabus gwaman, Muhammed Abubakar ranar laraba.
Lamarin nasa ya kara adadin manyan jami'an gwamnatin jihar Bauchi da suka aje aiki zuwa mutum uku.
A cikin watan Disamba na 2017, kwamishnan kasafin kudi da tsare-tsare, Shehu Ningi ya ajiye aiki sa. Daga baya shima mai baiwa gwamnan shawara kan ayyukan zuba jari, Samaila Sanusi ya sauka daga mukamin sa.
A labarin da jaridar Premiumtimes ta fitar, jami'an sun ajiye aikin su ne bisa rashin jituwa da yadda gwamnan yake gudanar da mulkin sa. Sun zargi gwamnan da yin kunnen kashi ga shawarwarin da suke bada wa wajen shugabantar jihar.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng