ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Makiyaya sun far ma sojoji, jami'ai biyu sun mutu

Sojojin sun nasarar kama mutum bakwai da ake zargi da sa hannu kan rikice-rikicen

Mai magana da yawun sojin Najeriya Birgediya Janar Texas Chukwu ya sanar da hakan inda ya bayyana cewa makiyayan sun bude ma ayayrin motocin sojojin wuta har tayi sanadiyar mutuwar jami'ai biyu.

"Wannan al'amari ya yi sanadiyyar mutuwar sojoji biyu. Amma tuni aka kama mutum bakwai da ake zargi da hannu a rikice-rikicen da ke faruwa" a cewarsa.

Ya kara da cewa a yayin da suke bincike, sojojin sun gano gawarwakin fararen hula 23 da suka mutu a garin Mararaba Dare wanda ke kusa da kauyen Rafiki yayin da suke sintiri, kuma wasu da dama sun jikkata.

Bugu da kari sakamakon harin sojoji biyu sun jikkata amma a kai su asibiti domin duba lafiyar su.

ADVERTISEMENT

Cikin makama da aka kama tare wadanda ake zargin akwai samfurin bindigar AK47 guda daya da harsasai da dama.

Rikici a jihar Filato

wannan lamarin ya biyo bayan kwanan iyu da samun labarin rikicin da ya barke a jihar Filato wanda yayi sanadiyar mutuwar mutum 25.

Ana zargi wasu makiyaya da gudanar da harin wanda yayi sakamakon mutuwar maza 19, mata 3 da yara 3.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT