Kawun Davido shine dan takarar gwamna na jam'iyar PDP
Gwamnan jihar Bayelsa Siriake Dickson ya jagoranci zaben kuma ya kaddamar dashi a matsayin dan takarar jam'iyar bayan yayi nasarar lashe zaben cikin gida.
Dan majalisar wanda yayi kaurin suna a dandalin sadarwa dangane da yawan tika rawa da yake yi a wajen taron biki ko nishadi zai ya lashe zaben jam'iya wanda aka gudanar ranar asabar 21 ga wata.
Ya lashe zaben ne da kuri'u 1, 569 cikin 3, 246 fiye da abokin takarar sa Akin Ogunbiyi,wanda ya samu kuri'u1, 562.
Gwamnan jihar Bayelsa Siriake Dickson ya jagoranci zaben kuma ya kaddamar dashi a matsayin dan takarar jam'iyar bayan yayi nasarar lashe zaben cikin gida.
Dangane da nasara da dan majalisar ya samu, tsohon gwamnan jihar Niger Alhaji Babangida Aliyu yace duk wanda bai gamsu da sakamakon zaben ya kai kara ga kwamitin daukaka kara na jam'iyar.
Sanatan zai fafata da yan takarar jam'iyar APC da SDC da ADC bayan sun kaddamar da jagororin su a zaben wanda za'a gudanar cikin watan Satumba na bana.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng