Za'a daura aurenta da angonta Ahmad Isa ranar asabar 14 ga watan afrilu da misalin karfe 1:00 na rana a masalacin al-manar dake garin kaduna.
Jaruma zata shiga sahu na gaba, zata shiga dakin aure
Za'a daura aurenta da angonta Ahmad Isa ranar asabar 14 ga watan afrilu da misalin karfe 1:00 na rana a masalacin al-manar dake garin kaduna
Jarumar ta wallafa hotun katin gayyata na daurin auren a shafin ta na Instagram tare da rubuta "Assalamu alaikum jama a ina gaiyatarku maza da mata zuwa wajan daurin aure na daza ai on 14th April ah masallacin almannar dake unguwan rimi kaduna ga wanda Allah yabashe ikon zuwa ngd".
Jarumar wacce ta rasa dan'uwar mahaifiyar ranar alhamis, ta sanar cewa an daga ranar taron biki zuwa mako mai zuwa.
"Innalillahi'wainna ilaihir rajiun Allah yayima yayar mamana rasuwa yau da safe dan haka za adaura aure na on 14th April ah masallacin almannar amma zamu daga taron biki sai next week insha Allah ina mai baku hakuri" ta rubuta a shafin ta.
Tauraruwar kamfanin White House tana daya daga cikin yan wasa da jarumi Adam Zango ya dauki nauyin fitowar su a masana'antar Kannywood.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng