ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

‘Ya kamata a dinga ɗaure barayin gwamnati a dajin sambisa’ - inji Magu

Shugabar huƙumar EFCC yayi kira da a kafa kurkuku a dajin sambisa don tsare masu laifin cin hanci da rashawa

Acting Chairman of the EFCC, Ibrahim Magu

Shugaban huƙumar yaki da cin hanci da rashawa na kasar nijeriya yayi kira da a kafa kurkuku a dajin sambisa don tsare masu aikata laifin zurmiya da cin hanci.

Bisa ga labarin da BBC hausa ta fitar, shugaban huƙumar yayi kiran lokacin da ake bikin bude offishin shiyya na huƙumar a kaduna.

Dajin sambisa maboya ce ta mayakan Boko haram a jihar Borno dake  arewa maso gabas na kasar.

“Muna kira da a kafa wata kurkuku a dajin sambisa don kawar da masu laifukan cin hanci da rashawa daga cikin mu” inji shugaban hukumar.

ADVERTISEMENT

Magu yayi kira ga bangaren shari’a da ta mara yunkurin gwamnatin tarayya wajen yaki da rashawa

“Dole mu canza lamarin da mu zage dumtsi wajen yakin masu neman gurgunta nasarar da muke samu’ yace.

Ya kara da cewa, “ dole mu hada karfi wuri guda don wankar da cin hanci da rashawa kafin ya kashe mu”.

A karshe Magu ya yi wa gwamnan jihar Kaduna Nasir El-rufai yabo don taimakon da ya ba huƙumar wajen bude offishin shiyya a jihar.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT