ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Gargadin da yan boko haram suka yi yayin da suka saki daliban Dapchi

Kamar yadda jaridar Associate press ta bayyana, yan ta'adar sun  ja kunnen al'ummar garin kan hana yan matan komawa makaranta

Bayan sama da mako hudu  da sace yan matan, mayakan sun dawo dasu daidai garin da suka sace su.

Kamar yadda jaridar Associate press ta bayyana, yan ta'adar sun  ja kunnen al'ummar garin kan hana yan matan komawa makaranta.

Wani shaidar gani da ido mai suna Mohammed Ali ya bayyana ma manema labaran NAN cewa yan ta'addar sun bayar da shawara na a aurar dasu.

Yana mai cewa " Su da kansu suka mayar da yan matan. sai da ma na gaisa da wasu gud biyu daga cikin su. matasa ne masu kwazo sai dai suna tare da makamai. Sun yi mana gargadi na kada mu bari yan matan su koma makaranta. Shawarar da suka bayar shine na a yi masu aure."

ADVERTISEMENT

Yawon yan matan da aka saki

Kan batun dawowar su gwamnatin tarayya ta bayyana cewa kididdigin da aka gudanar ya tabbatar cewa yan matan su 104 a dawo dasu tare da wani yaro.

Sai dai har yanzu akwai sauran mace daya daga cikin yan matan a hannun mayakan kuma dalibai biyar sun rasu daga cikin yan mata 110 da aka sace.

kamar yadda daya daga cikin yan matan da aka saki ta bayyana, an cigaba da rike daya daga cikin su domin taki amincewa ta sauya addinin zuwa musulunci.

Enhance Your Pulse News Experience!

Get rewards worth up to $20 when selected to participate in our exclusive focus group. Your input will help us to make informed decisions that align with your needs and preferences.

I've got feedback!

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT