ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Minista yace boko haram na neman watsa ma gwamnatin Buhari kasa a ido

Ministan ya bayyana hakan ne yayin da kai ziyarar gani da ido jihar Yobe ranar alhamis 22 ga wata domin ganin yadda al'ummar jihar ke fama da sakamakon harin da yan ta'addar suka kai.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin da kai ziyarar gani da ido jihar Yobe ranar alhamis 22 ga wata domin ganin yadda al'ummar jihar ke fama da sakamakon harin da yan ta'addar suka kai.

A yammacin ranar litinin 19 ga wata ne yan ta'adda da ake zargin cewa yan boko haram ne suka far ma garin Dapchi inda har suka awon gaba da yan matan makaranta tare da sace wasu kayan abinci a cikin garin.

Yayin da ya zanta da manema labaraia a daidai makarantar yan matan da aka sace, ministan ya kara da cewa gwamnatin tarayya tana iya bakin kokarin ta wajen kawo karshen ta'addancin kungiyar tare da yin la'akari na cewa harin da suka kai yankin yana iya zamantowa borin kunya kasancewa sojoji sun fatattaki asalin gidauniyar su dake nan dajin sambisa.

A cewar sa sauran kiris a kawo karshen kungiyar bisa ga kokarin da jami'an tsaro keyi wajen ganin hakan ya faru.

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT